Connect with us

Labarai

Rundunar Civil Defence za ta baza jami’ai 1,350 yayin bukukuwan kirsimeti a jihar Kano

Published

on

Rundunar tsaron Civil Defence a jihar Kano ta ce ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara a fadin jihar.

 

Mai magana da yawun hukumar, Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana hakan a zantawarsa da freedom radio.

Ya ce rundunar za ta fitar da jami’ai  1,350, domin tsaron wuraren ibada, kasuwanni, da wuraren shakatawa a duk fadin jihar, domin tabbatar da komai na tafiya cikin kwanciyar hankali ba tare da samun wata matsala ba.

Rundunar ta Civil Defence ta kuma bukaci ƙarin haɗin kai daga al’umma, domin dakile ayyukan masu barnata kayan gwamnati da ma kadarorin da aka samar don cigaban ƙasa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!