Connect with us

Labarai

Rundunar yan sanda ta hana jami’an KAROTA da na Vigilante zuwa wajen zaɓe

Published

on

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta haramta wa jami’an KAROTA da ’yan sa-kai na kungiyar Vigilante, shiga wuraren zaɓe a yayin zaɓen cike gurbi da za a gudanar a kananan hukumomin Ghari, Tsanyawa, Bagwai da Shanono a gobe Asabar, 16 ga watan Agusta, 2025.

 

Rundunar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a daren jiya Alhamis a madadin kwamishinan ’yan sanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori.

 

Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne tare da sauran matakan tsaro domin gudanar da zaɓen cikin lumana, adalci da gaskiya.

 

Ta kuma bayyana cewa zirga-zirgar motocin hawa, Adaidaita Sahu da babura za a takaita su daga ƙarfe 12:00 na tsakar daren Juma’a zuwa ƙarfe 6:00 na yamman ranar zaɓen, sai dai ban da  motocin ayyukan gaggawa, motocin hukumar zaɓe da masu sa ido da aka amince da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!