Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar ‘yan sanda ta Kano ta yi holin masu yin garkuwa da mutane

Published

on

Rundunar ‘yansandan ta jihar Kano tayi holin wasu mutane da take zargi da laifukan  yin garkuwa da mutane da yin fashi da makami, da kuma satar ababan hawa da kuma safarar miyagun kwayoyi a jihar Kano.

Sabon Komishinan ‘yansandan na jihar Kano CP Habu Ahmad Sani, ya sanar da hakan yayin da yake holen kayayyakin laifukan da kuma mutane da ake zargi a yau Laraba a shelkwatar rundunar ‘yan sanda dake nan

Kazlika kwamishinan ‘yan sandan Habu Ahamad Sani, ya ce  rundunar zata cigaba da kama masu laifi a duk inda suke don  ganin zaman lafiya ya wanzu a jihar Kano da ma kasa baki daya.

Kano: Lauyoyi sun yi barazanar gurfanar da kwamishinan ‘yan sanda

Jihar Kano ta sami sabon kwamishinan ‘yan sanda

Rundunar ‘yan sandar jihar Kano ta sake ceto wani yaro a Anambra

Wasu  daga cikin wadanda ake zargin sun yin a dama yayin da kuma wasu daga ciki ke bayyana irin dalilan da ya sanya jami’an ‘yan sandan suka kama su.

Har ila yau wasu daga cikin wadanda ake zargin sun ce sun taka sahun barawo ne amma kuma sun na damar aikata hakan.

A hannu guda kuma wasu ana zargin su ne da siyan kayayyakin sata.

Wakilin mu Abba Isah ya ruwaito cewa komishinan ‘yansandan Kano Habu Ahmad Sani, ya yi kira ga alummar jihar Kano da dinga tallafawa jami’an tsaro ganin lamarin tsaro na bukatar masu ruwa da tsaki kuma na kowa da kowa ne, a don haka na bukatar gudunmawar kowa da kowa.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!