Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar Yan sandan Kano ta karbi bindigogi da albarusai 60 da mutanen ke rike da su ba bisa kaida ba suka mika mata

Published

on

Rundunar Yansanda ta jahar Kano ta karbi bindigogi da albarusai guda 60 daga hannun mutane da suka mika da kansu domin yin biyayya ga umarnin babban sufeton Yan sanda Ibrahim Idris.

Kwamishinan Yan sanda na Jihar Kano Rabiu Yusuf ne ya bayyana hakan ga manema labarai a matakin da rundunar ta dauka nakira ga mutane su mika makaman dake hannunusu da su ka mallaka ba bisa kaida ba.

Yace bindigogin da albarusan da aka mika yau an samo su ne daga hannun mutane da suka bi umaranin mika makamai da suka mallaka ba bisa kaida ba.

Kwamiuhinan Yanasanda Rabiu Yusuf yace mika makaman hanya ce ta kawar da makamai da jamaa suka mallaka ba bisa kaida ba kafin zaben 2019.

Rabiu Yusuf ya kuma gargadi cewa duk wanda yaki ya mika makaman da ya mualaka ba bisa kaida ba kuma aka kamashi doka zata yi aiki  a kansa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!