Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Saɓa ƙa’ida: An rufe kamfanoni 4 na ƴan China a Kano

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta rufe wasu kamfano 4 mallakin ƴan kasar China da ke sarrafa ledar da aka yi amfani da ita.

An rufe kamfanin sakamakon zarginsu da gudanar da aiki ba bisa ƙa’ida ba.

Jami’in kula da harkokin kasuwanci na ma’aikatar masana’antu da kasuwanci ta jihar Kano Adamu Umar ne ya jagoranci gudanar da rufe kamfanonin.

Da yake jawabi ga manema labarai mataimakin shugaban kungiyar Kwadago ta ƙasa NLC reshen jihar Kano Kwamared Ado Salisu Riruwai ya ce “kamata ya yi a ce ƴan asalin Jihar Kano ne suka mallaki irin waɗannan kamfanoni”.

A na sa bangaren shugaban kungiyar masu sana’ar tara robobi da kwalaye da aka yi amfani da su Kwamared Salisu Ali Yarima ya yabawa matakin gwamnati na rufe kamfanonin.

“matakin da gwamnatin jihar Kano ta ɗauka na rufe kamfanonin ƴan China zai ba da dama ga ƴan kasa su kafa nasu tare da bunƙasa tattalin arziki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!