Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Wani Sabon gidan abincin Naira Talatin ya hana wasu Almajirai bara a Kano.

Published

on

Daliban Tsangaya

A unguwar Sani Mainagge,sakamakon sake bude gidan abinci na Naira talatin gidaje dake makwabtaka da gurin sun fara sauke tukwanansu.

Biyo bayan maganar da minstan noma Alhaji Sabo Nanono yayi, a game da abincin Naira talatin ,wanda sakamakon hakan ya saka aka bude gidan abincin a unguwar Sani Mai Nagge.

Sai ga shi wani mai gyaran Rediyo  ya samu karfin giwa inda shi ma ya bude gidan abincin na Naira 30.

Wanda ya bude gidan ya shaidawa Freedom Radio cewa sakamakon bude gidan abincin na Naira talatin makotansa sun sauke tukwane saboda saukin abincin sa.

Haruna Injinya ya kara da cewa makotan nasa kan turo yara biyar da Naira dari da hamsin domin sayan abinci.

Haruna mai sabon gidan abincin na Naira 30 ya kara da cewa a rana yana dafa shinkafa buhu daya da wake rabin buhu da garin kwaki buhu daya.

Ya kara da cewa wasu na zuwa gidan abincin domin saye a rabawa mabukata.

A nata bangaren mai dakin da ya bude sabon gidan abincin Hajiya Sadiya Saidu ,ta ce hatta Almajiran unguwar na zuwa sayan abincin na Naira talatin.

Ta kara da cewa hakan ta sa Almajiran sun daina bara sai dai su nemo Naira talatin domin sayan abincin.

 

 

 

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!