Labarai
Sama da mutane dubu biyar ne suka rasa muhallan su a ambaliyar ruwan Neja

Izuwa yanzu sama da mutane ɗari ne suka rasa rayukansu yayin da sama da dubu biyar suka rasa muhallan su a ambaliyar ruwan da ta auku a Mokwa dake Jihar Neja.
Sakataren yaɗa labaran Ƙaramar Hukumar Mokwa Abdullah Abubakar Dakani ne ya shaida hakan ga Freedom Rediyo.
Ya ce tuni aka tsugunar da mutanen da amabaliyar ruwa ta shafa a makarantun firamari dake makotaka da yankin, karkashin kulawar Gwamnatin Jihar da
Hukumar bayar da agajin gaggawa da sauran Hukumomim da abin ya shafa.
You must be logged in to post a comment Login