Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Samar da masana’antu a Arewacin ƙasar nan zai bai wa matasa ayyukan yi – Farfesa Murtala Sagagi

Published

on

Masanin tattalin arziki a makarantar koyar da harkokin kasuwanci a jami’ar Bayero anan Kano ya ce, samar da wadatattun masana’antu a Arewacin ƙasar nan rage marasa aikin yi.

Farfesan Murtala Sabo Sagagi ya ce, yin hakan zai taimaka wajen rage matasan da ke zaune babu abin yi a yanzu.

Farfesan Sagagi ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala shirin “Barka da Hantsi”na nan Freedom Radio.

Ya ce, idan har ana son samar da yanayi mai kyau a kasar nan, to kuwa sai gwamnati ta gyara tsarin masana’antu da harkokin tafiyar da su.

Murtala Sabo Sagagi Ya ƙara da cewa idan da gwamnati za ta riƙa ciyo bashi tana sakawa cikin masana’antu to kuwa yankin Arewa zai zarce kudancin ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!