Labarai
Sarki Muhammadu Sanusi II ya goyi bayan dasa bishiyu don yaƙi da kwararowar hamada

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga hakimai, dagatai da masu unguwanni da su ƙara himma wajen dasa bishiyoyi domin rage illar kwararowar hamada.
Sarkin ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da dashen bishiyoyi a fadarsa da ke Kofar Kudu, inda ya jaddada muhimmancin bishiyoyi wajen samar da iska mai kyau da kare muhalli.
A nasa bangaren, Kwamishinan Ruwa da Muhalli na Jihar Kano, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya ce gwamnati na shirin dasa bishiyoyi sama da miliyan 10 a ƙananan hukumomi 44 na jihar domin magance matsalar kwararowar hamada.
You must be logged in to post a comment Login