Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarkin askar Kano ya kalubalanci likitoci akan yi wa maza shayi

Published

on

Sarkin Askar jihar Kano Ahaji  Dakta na Bango ya kalubalanci likitoci akan su daina sukar salon yi wa maza shayi da suke yi su.

Alhaji Dakta na bango ya bayyana hakan ne a yayin da ya kira taron manema Labarai domin nuna takaicinsa  kan  irin kallon raini da Likitoci suke yiwa sana`arsu.

A cewar sa sun gada ne tun iyaye da kakanni  ba wai da rana tsaka kawai suka shiga sana`ar ba.

Sarkin Kano ya bukaci masu rike da sarautun gargajiya su yi aiki kafada-da-kafada da hukumar ilimin manya

Ka zalika sarkin Askar ya bayyana bambamcin sana`ar tasu da ta likitoci yana mai buga misali da bambancin Kazar gida da Kazar gidan gona.

Na Bango ya  kara da cewa a kasashen da aka cigaba likitan turawa  basa sukar masu magugunan gargajiya,ko kuma su kan su  masu maganin gargajiya su soki magugunan turawa.

Yana mai cewar akan haka ya zama wajibi likotoci su dena sukar kai tsaye su don kuwa su basa yi.

Sarkin Askar ya kara da fadar bambanci akan shayi,inda yace shayi ya kasu a kalla kala Goma, kuma  bambanci sosai a tsakanin Shayin asibiti da na gargajiya.

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!