Labarai
Sarkin Kano Sunusi na II ya kalubalanci aurar da yara mata kanana

Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi na II, ya yi kakkausar suka kan duk wani nau’i na cin zarafi ga mata da kuma auren ƙananan yara, yana mai jaddada cewa al’ada ba ta ba wa kowa ikon dukan mace ko tauye mata haƙƙinta.
Sarkin ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels, inda ya ce dukkan ’yan Najeriya suna da kariya a ƙarƙashin doka, ba tare da la’akari da al’ada ko yankin da suka fito ba.
Sarki sunusi ya ce yawancin abubuwan da ake jingina wa al’ada a matsayin dalilin cin zarafi, a zahiri sakamakon talauci ne, rashin daidaiton iko tsakanin maza da mata, da kuma gazawar gwamnati wajen samar da muhimman ayyuka.
Game da auren yara, Sarkin ya ce matsalar ta fi fitowa fili a yankunan karkara, inda ’yan mata ke kammala firamare tun suna da kusan shekara 11 ba tare da samun damar zuwa sakandare ko koyon sana’a ba.
Duk da haka, Sarkin ya jaddada cewa dole ne Najeriya ta tsaya kan ƙa’idoji da doka, yana mai cewa duk wani nau’i na cin zarafi ga mata da yara ba abin yarda ba ne.
You must be logged in to post a comment Login