Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarkin Katsina na Shirin korar Shirin AGILE daga jihar

Published

on

Mai Martaba Sarkin Katsina, Abdulmuminu Kabir, na shirin korar shirin nan na inganta ilmin ’yan mata mai suna AGILE daga fadin jihar.

 

Sarkin ya ce, shirin na AGILE yana wuce gona da iri da kuma kokarin gurbata tarbiyyar Musulunci da ta al’ada da aka san yankin da ita.

 

Sarkin ya bayyana haka ne a fadarsa ranar Asabar lokacin da yake aiwatar da wasu nade-nade.

 

Kazalika, ya ce shirin yana cin karo da koyarwar addinin Musulunci wanda ya ce a matsayinsu na iyayen al’umma ba za su bari hakan ta faru ba.

 

Don haka ya ce, lallai ne wannan shiri ya fita daga Jihar Katsina baki daya.

 

Shiri AGILE na da nufin habaka ilmin zamani na ’yan mata daga karamar makaratun sakandaren zuwa babba, inda ma har ake ba su wani ihisani.

 

Sai dai wasu masu nazari da suka yi sharhi a kai sun ce shirin in baya ga bata tarbiyya da kokarin sanya daliban bujire wa iyaye da wasu ka’idodi da tarbiyar addini da ta al’ada babu abin da shirin yake koyarwa.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!