Connect with us

Labarai

Sarkin Kano ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Published

on

Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi fitaccen malamin addinin Musulunci  Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a satin daya gabata.

‎Sarkin ya bayyana rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi a matsayin babban rashi ba wai kawai  ga iyalan sa kadai ba har ma ga daukacin al’ummar musulmi gaba daya.

‎Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya ce  rasuwar ta bar gibi babba da zai yi wahala a cike  duba da irin gudummawar da Shehin Malamin  ya bayar wajen hade kan al’umma da bunkasa addinin Musulunci.

‎A nasa jawabin babban ɗan marigayin Sheikh Ibrahim Dahiru Usman Bauchi, ya yi godiya ga Sarkin  bisa ta’aziyyar  tare da yi wa Sarkin addu’ar samun nasara da jagoranci cikin adalci.

‎Wakilin mu na masarautar Kano Shamsu Dau Abdullahi,  ya rawaito cewa Sarkin na tare da rakiyar manyan hakimai na masarautar Kano da suka hada da wazirin Kano Alhaji Sa’adu Shehu Gidado,  Galadiman Kano Alhaji Mannir Sanusi, da Madakin Kano Alhaji Yusif Nabahani Cigari da Kuma manyan jigajigan  darikar Tijjaniyya na nan Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!