Connect with us

Addini

Sarkin Musulmi ya ayyana Laraba a matsayin daya ga Zul-hijja

Published

on

Mai alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya ayyana yau Laraba, 28 ga watan Mayu da muke ciki a matsayin ranar daya ga watan Zul-hijja na shekarar 1446 bayan Hijira.

 

Sarkin Musulmin, wanda shi ne shugaban Majalisar kolin addinin Musulunci, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta babban mashawarcinsa na musamman kan harkokin addini Farfesa Sambo Wali Junaidu ya sanya wa hannu.

 

Wannan sanarwa dai na nufin za a yi idin babbar Sallah a Najeriya a ranar Juma’a 10 ga watan na Zul-hijja, wadda ta yi dai-dai da 6 ga watan Yunin bana.

 

Wannan dai na zuwa ne dai-dai da ganin watan a kasar Saudiyya, wadda tun farko ta ayyana Laraba a matsayin ranar daya ga watan na Zul-hijja, tare da cewa za a hau Arfa a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!