Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Saudi Arabia ta kawo karshen wasanni 36 da Argentina ke samun nasara

Published

on

Tawagar kwallon kafar kasar saudiya ta doke kasar Argentina a wasan farko na gasar cin kofin duniya a kasar Qatar da ci biyu da daya a yau Talata a rukuni C.

Kyaftin din tawagar Argentina Lionel Messi ne ya fara saka kasar tasa a gaba, a bugun daga kai sai mai tsaron raga a mintuna na goma.

Sai dai mintuna uku bayan dawowa daga hutun rabin lokaci kasar ta Saudia ta warware kwallon ta hannun Al- Shehri kana dan wasa Al-Dawsari ya zura kwallo ta biyu a minti na 53 wanda hakan ya basu  nasarar farko a gasar ta bana.

Kasar ta Argentina na cikin jerin kasashen da ake saka ran zasu lashe gasar ta Duniya a bana.

Wannan shi ne karon farko da kasar ta saudia ta samu nasara a wasan ta na farko.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!