Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

SERAP ta yi barazanar gurfanar da ‘yan majalisu da gwamnoni a gaban kotu

Published

on

Kungiyar da ke rajin tabbatar da daidaito da gaskiya a ayyukan gwamnati SERAP ta yi barazanar gurfanar da majalisun dokokin tarayyar kasar nan da kuma kungiyar gwamnonin arewa matukar aka aiwatar da dokar sanya idanu kan kafafen sada zumunta.

Kungiyar ta SERAP ta bayyana hakan ne ta cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na twitter.

A cewar kungiyar ya zama wajibi ta dauki wannan mataki don dakile yunkurin da gwamnonin arewa da kuma majalisun dokokin tarayya ke yi don kafa dokar da za ta takaita ‘yancin da ‘yan kasar nan ke da shi a shafukan sada zumunta.

Tun farko dai gwamnonin na arewa yayin wani taro da suka gudanar jiya a Kaduna, sun ce, daukar wannan mataki ya zama wajibi saboda yadda aka yi amfani da shafukan sada zumunta don yada karairayi yayin zanga-zangar kin jinin ‘yan sandan SARS.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!