Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shiga yajin aiki saɓa alƙawarin da muka yi ne – Martanin Gwamnati ga likitoci

Published

on

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da shirin tsunduma yajin aikin na ƙungiyar likitoci a yau Litinin.

A wata sanarwa da ma’aikatar Ƙwadago ta ƙasa ta fitar, a yammacin Lahadi, ta ce Gwamnatin tarayya tana bin yarjejeniyar da suka ƙulla da ƙungiyar a ranar 21 ga watan Agustan da muke ciki.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun jami’in yaɗa labaran ma’aikatar Charles Akpan ta ce, matakin da likitocin suka ɗauka ya saɓa da abin da aka cimma a yarjejeniyarsu da Gwamnati a baya.

Mista Akpan ya ce, Gwamnatin tarayya na aiwatar da ɓangarenta na yarjejeniyar tare da sanya idanun ministan ƙwadago. A yau Litinin ne ƙungiyar likitocin ta ƙasa ta ayyana shiga yajin aikin gargaɗi na makonni uku. Shugaban ƙungiyar na ƙasa Farfesa Innocent Ujah ne ya sanar da hakan, bayan babban taronta na ƙasa a birnin Benin na jihar Edo.

Ƙungiyar likitocin ta ce, tsunduma yajin aikin ya zama dole, sakamakon gaza cimman buƙatunta da Gwamnatin tarayya ta yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!