Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari zai tafi Ghana domin halartar taron ƙoli na shugabannin yankin tekun Guinea

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tafi kasar Ghana domin halartar taron ƙoli na shugabannin ƙasashen yankin tekun Guinea da za a gudanar a Accra babban birnin ƙasar.

A cikin wani saƙo da fadar shugaban ƙasar ta wallafa a shafinta na Tuwita, ta ce, shugaban zai bar gida Najeriya a yau Talata, inda shugaban ƙasar Ghana Nana Akuffo-Ado zai jagoranci taron.

Ana sa ran shugaban zai gabatar da jawabi a taron wanda zai tattauna dabarun ƙarfafa zaman lafiya da tsaro da yaƙi da masu aikata miyagun laifuka a gaɓar tekun yankunan ƙasashen.

Yayin halartar taron, shugaban zai samu rakiyar ministan harkokin ƙasashen waje Geoffrey Onyeama, da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Babagana Monguno mai ritaya, da daraktan hukumar tattara bayanan sirri Ambasada Ahmed Rufai Abubakar, da sauran jami’an gwamnati.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!