Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a fara kwashe Yan Nijeriya daga Sudan- NEMA

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta tabbatar da cewa daga gobe Talata za ta fara kwaso ‘yan Nijeriya sama da dubu biyu da ke makale a kasar Sudan mai fama da rikici da ya yi sanadiyyar mutuwar daruruwan mutane.

Daraktan ayyukan na musamman a hukumar Olamide Bandele ne ya sanar da hakan lokacin da yake tattaunawa da gidan Talabijin na Channels kai tsaye a yau litinin.

Olamide Bandele ya ce yanzu haka babban Daraktan hukumar ta NEMA Mustapha Habib yana birnin Alkahira na kasar Egypt, inda suka tanadi motocin da za su kwashi ‘yan Najeriyar.

A jiya Lahadi ne dai ministan harkokin wajen kasar nan Geoffrey Onyeama ya shaidawa gidan Talabijin na Channels cewa wadanda za a kwaso sun kai dubu biyar da dari biyar, kuma kashi tamanin cikinsu dalibai ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!