Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya sauka a kasar Kenya don halartar taron koli

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya isa birnin Nairobi na kasar  Kenya don halartar taron kolin Afirka da Faransa da aka shirya gudanarwa tsakanin yau da gobe.

 

Taron mai taken “Afirka ta ci gaba: Haɗin gwiwar Afirka da Faransa don kirkire-kirkire da ci gaba,” zai tattauna kan muhimman batutuwan da suka shafi nahiyar, ciki har da sauyin makamashi, masana’antu masu zaman kansu, ayyukan sauyin yanayi da kuma gyare-gyaren tsarin kuɗaɗen duniya.

 

Daga cikin waɗanda suka tarbi shugaba Tunibu akwai Ministan Masana’antu da Zuba Jari, Dakta  Jumoke Oduwole da  Ministan Muhalli Balarabe Abbas Lawal da  Ministan Noma da Tsaron Abinci  Sanata Abubakar Kyari da Ministan Harkokin Waje  Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu da  Ministan Harkokin Waje Ambasada Sola Enikanolaye.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!