Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Shugaban Turkiyya Recep Tayyib Erdogan ya janye barazanar korar jakadun kasashe 10

Published

on

Shugaban Turkiyya Recep Tayyib Erdogan ya janye barazanar sa na korar wasu jakadun kasashen Turai 10 sakamakon zargin su da matsawa gwamnatin sa lamba.

Musamman na sakin wani dan gwagwarmaya da gwamnatin ta kama.

Tun a Litinin din makon jiya ne Erdogan ya yi barzanar sallamar jakadun kasashen Canada, Denmark, France, Germany, Netherlands Norway Sweden Finland, Newzealnad da Amurka, bisa zargin su da hada baki wajen yi wa kasar zagon kasa.

Duk da cewa ana ganin Erdogan ya yi amai ya lashe kan batun sallamar jakadun, ba kuma tare da ya bada wasu hujjoji ba, ya gargade su da su yi taka tsan-tsan.

Kafin Erdogan ya bada sanarwar sai da majalisar zartaswar kasar ta tattauna batun sallamar jakadun, inda ta ce kai tsaye suna katsalandan ne ga zaman lafiya da kuma tsare-tsaren kasar.

Kasar ta Turkiyya wadda mamba ce a kungiyar tsaro ta NATO ta jima tana samun rashin jituwa da kasashen turai, saboda banbancin ra’ayi irin na siyasa.

rfi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!