Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Dokar Tilastawa mutane nuna shaidar rigakafin Korona ta soma aiki a Tunisia

Published

on

Gwamnatin Tunisia ta ce daga yanzu ya zama dole dukkanin ‘yan ƙasar da kuma baƙi su nuna shaidar karbar allurar rigakafin cutar COVID-19 kafin shiga wuraren tarukan jama’a.

Karkashin dokar da shugaba Kais Saed ya sanar a Juma’ar da ta gabata, ana bukatar manyan jami’ai da sauran ma’aikata su nuna katin dake tabbatar da sun yi allurar rigakafin cutar Korona.

Wannan ne zai ba su damar gudanar da ayyukansu a ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu.

Har ila yau, za a bukaci shaidar rigakafin kafin shiga gidajen abinci, otal-otal da wuraren yawon shakatawa.

Sabuwar ta Tunisia ta kuma nuna cewar za a dakatar da ma’aikatan da ba su yi allurar rigakafi ba a ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu, har sai sun gabatar da shaidar.

 

rfi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!