Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Shugabancin hukumar AFN ya dare gida biyu

Published

on

Mutane biyu na ikirarin lashe zaben shugabancin hukumar wasan guje-guje da tsalle-tsalle ta kasa AFN da aka gudanar daban-daban.

An dai gudanar da zaben ne a ranar Litinin 14 ga watan Yuni, inda Shehu Gusau da kuma Tonobok Okowa kowane ke ikirarin cewa shi ne zababben shugaban hukumar ta AFN.

Hukumar ta kasance cikin rikicin shugabanci tun a shekarar 2019 sakamakon ‘yancin cin gashin kai da zababben shugaba na shekarar 2017 Shehu Gusau ya nema daga hannun ma’aikatar wasanni ta kasa.

Hakan ne ya sanya aka raba gari tsakanin shugaban hukumar Shehu Gusau da mataimakinsa Olamide George kowa na cewa shi ne shugaban hukumar.

An dai rantsar da shugabannin bangarorin biyu da zummar kama aiki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!