Connect with us

Labarai

Sojoji sun hallaka jagoran ƴan bindiga Junaidu Fasagora

Published

on

Dakarun sojin Nijeriya da ke gudanar da aikin yaƙa da yan ta’adda a jihar Zamfara, sun kashe gawurtaccen jagoran ƴan bindigar nan Junaidu Fasagora tare da wasu yaransa.

Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a kafar Internet.

Sanarwar ta ruwaito cewa dakarun sun samu wannan nasara ne bayan da suka fafata ta hanyar yin musayar wuta da bata garin a yankin ƙaramar hukumar Tsafen jihar Zamfara.

Haka kuma, sanarwar, ta bayyana cewa, “Junaidu Fasagora tare da sauran ƴan bindiga abokansa sun dade suna garkuwa da mutane tare da aikata wasu ayyukan ta’addanci ga al’ummar jihohi da dama na yankin arewa maso yammacin kasar.”

“Wannan gagarumar nasara ce a yaƙin da ake yi da ta’addanci da kuma rashin tsaro” in ji sanarwar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!