Connect with us

Labarai

Sojoji sun kama wani kasurgumin dan kunar bakin wake a jihar Borno

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun kama wani mutum da ake zargin ɗan ƙunar baƙin wake ne a Jihar Borno, tare da ƙwace kayayyakin da ake amfani da su wajen haɗa bam.

Rundunar ce ta sanar da hakan a shafinta na X.

Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ɗan asalin ƙaramar hukumar Bama ne, kuma an gano yana da wasu ƙarin kayayyaki ko makamai masu alaƙa da ayyukan ta’addanci.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, laftanar kanar Sani Uba, ya ce an same wanda aka kama ɗin da kayayyakin bama-bamai da aka riga aka haɗa, abin da ke nuna shirin kai hari.

Rundunar ta ce, a halin yanzu wanda ake zargin yana hannun jami’an tsaro domin zurfafa bincike don gano masu ɗaukar nauyinsa da abokan aikinsa da kuma alaƙarsa da ƙungiyoyin ta’addanci a yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!