Labarai
Sojoji sun yi nasarar kashe Yan ta’adda da dama a Zamfara

Rundunar sojin Najeriya, ta ce dakarunta sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama a yaran ƙasurgumin ɗan bindiga Ado Aleiro a wata arangama da suka yi a ƙaramar hukumar Tsafe da ke jihar Zamfara.
Gidan talabijin ta Channels ya ruwaito cewa an fara arangamar ne tun a ranar Asabar da yamma lokacin da ɓarayin dajin suka kai wa ‘yan sa-kai hari a ƙauyen Kunchin Kalgo hari.
Daga cikin waɗan da rahotanni ke cewa an kashe akwai Kachalla Iliya Sarki, wanda aka ce ɗa ne ga ƙasurgumin shugaban ɓarayin daji Ado Aleiro, tare da wani babban ɓarawon daji mai suna Dogo Bete.
You must be logged in to post a comment Login