Connect with us

Labarai

Sojojin Amurka 100 sun iso Najeriya don taimakawa wajen yaƙi da ƴan ta’adda

Published

on

Shalkwatar tsaro ta tabbatar da isowar sojojin Amurka su  100,  don taimaka mata a yaƙin da ta ke da ƴan ta’addar da ke kaiwa jama’a hare-hare.

 

Kakakin shalkwatar tsaron kasar nan  Manjo Janar Samaila Uba ne ya bayyana hakan  da ya ce Sojin na Amurka, ba  za su shiga fagen daga don yin yaƙi ba,  sai dai zasu gudanar da  aikin horar da dakarun kasar nan  na dabarun yaƙi da ƴan ta’adda.

 

Zuwan na sojojin Amurka ya biyo bayan tun farko Donald Trump ya zargi kasar nan  da gazawa wajen baiwa Kiristoci kariya daga hare-haren da ‘ƴanta’addan da ya kira da Musulmai ke kaiwa a sassan ƙasar.

 

Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargin bayan da ta ce ƴan ta’addan na kashe dukkanin ɓangarorin Musulmai da kuma Kiristoci kuma dakarunta na aiki tuƙuru wajen yaƙi da su musamman a yankin arewa maso yammaci da kuma arewa maso gabas.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!