Ƙetare
Sojojin Amurka na shirin kutsawa Iran ta kasa

Jaridar Washington Post ta bayar da rahoton cewa ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon na shirin tura sojojin ƙasar domin shiga Iran ta ƙasa don yin yaƙi na makonni.
Sai dai jaridar ta ambato wasu jami’ai na cewa babu tabbaci ko Shugaba Trump zai sahale wa buƙatar tura sojojin ta ƙasa.
Rahoton ya ce shirin ya nuna shigar sojojin ta ƙasa ba zai zama cikakkiyar mamaya ba, sai dai yawaita samame haɗe da yaƙi ta ƙasa.
Amurkawa sun yi imanin cewa sojojin ƙundunbalan ƙasar fiye da 4,000 ne suka nufi yankin Gulf, yayin da ake tattauna batun ƙari.
You must be logged in to post a comment Login