Ƙetare
Sojojin Isra’ila sun ƙaddamar da hari mafi muni a Lebanon

Ministan lafiya na Lebanon ya ce daruruwan mutane ne suka jikkata wasu kuma suka mutu a sassan kasar, bayan da sojojin Isra’ila suka kaddamar da mafi munin hare-hare, tun bayan ɓarkewar sabon rikici tsakanin su da ƙungiyar Hezbollah.
Ministan ya ce asibitoci sun cika makil da waɗanda suka jikkata.
An kai hare-haren ne a yankuna da suka haɗa da Beirut da Sidon, inda rundunar sojin Isra’ila ta ce farmakin ya kasance mafi kyau da aka kai kan cibiyoyin Hezbollah da kayayyakin soji sama da Ɗari.
Babban hafsan sojin Isra’ila ya ce rundunar IDF za ta ci gaba da kai hare-hare kan Hezbollah, duk da cewa Pakistan wadda ta shiga tsakani wajen samar da tsagaita wuta da Iran, ta ce wannan bangaren na yakin shi ma za a dakatar da shi.
A baya dai, ƙungiyar Hezbollah ta bukaci magoya bayanta da su kara hakuri da juriya da kuma jajircewa.
You must be logged in to post a comment Login