Ƙetare
Faransa ta yi watsi da juyin mulkin Nijar
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/07/Flag-France.jpg)
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta ce, kasar ba ta amince da ikirarin da dakarun sojin Nijar suke yi ba na karbe Iko a kasar bayan hambarar da Gwamnatin Bazoum, inda tace haryanzu a bangaren ta Muhammed Bazoum din ne halastaccen shugaban Jamhuriyar Nijar.
A cewar Faransa Bazoum shine mutumin da al’umma Nijar suka zaba, a don haka tace basu amince da kifar da gwamanatin farar hula da sojin sukai ba, inda tabi sahun sauran kasashen Duniya na kiraye-kirayen ayi gaggawar mayar da kasar hannun farar hula.
You must be logged in to post a comment Login