Labarai
Tajudeen Abbas ya rushe dukkan kwamitocin wucin-gadi na Majalisar Wakilai

Shugaban majalisar wakilai Tajudeen Abbas, ya bayar da umarnin rushe dukkan kwamitocin wucin-gadi na Majalisar.
Matakin ya fara aiki daga ranar 28 ga Agusta, 2026, bayan wa’adin da aka bai wa kwamitocin ya kare.
Majalisar ta ce an bai wa kwamitocin wa’adin kammala ayyukansu da gabatar da rahotanni, amma lokacin ya wuce.
An kuma umarci shugabannin kwamitocin da su mika duk wasu rahotanni da takardun da suka rage ga ofishin magatakardar Majalisar.
Daga yanzu, duk wani aiki da ake yi da sunan kwamitocin da aka rushe ya kamata ya tsaya.
You must be logged in to post a comment Login