Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya bukaci shugabanni su fifita bukatun al’umma kan bukatun kansu 

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci shugabanni a matakai daban-daban da rika fifita bukatun al’umma kan bukatun kansu. 

 

Tinubu ya ce Najeriya na bukatar shugabanni masu kishin kasa, wadanda za su sadaukar da kansu wajen yi wa al’umma hidima da kuma kawo ci gaba.

 

Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen bikin cika shekaru 70 da haihuwa na tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, da aka gudanar a Yola, Jihar Adamawa.

 

Tinubu, wanda sakataren gwamnatin tarayya George Akume, ya wakilta, ya ce ya kamata shugabanni su dauki matakin hidimtawa al’umma da ci gaban kasa a matsayin babban abin da ya fi muhimmanci.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!