Connect with us

Labarai

Tanzania: Masu zanga-zanga sun sake mamaye kan tituna

Published

on

Masu zanga-zanga sun sake fitowa kan tituna a Tanzaniya karo na uku, duk da gargadin da hafsan sojin kasar ya yi musu na su dakatar da tarzomar da rikici.

Zanga-zangar ta barke a manyan birane inda matasa ke nuna adawa da sakamakon zaben da aka gudanar ranar Laraba, suna cewa ba a yi adalci ba domin an hana manyan ‘yan adawa yin takara da shugabar kasa Samia Suluhu Hassan.

Har yanzu intanet ɗin kasar a katse yake, abin da ke hana samun sahihan bayanai kan mutuwar mutane, yayin da hukumomi suka tsawaita dokar hana fita domin rage tarzomar.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira ga jami’an tsaro na kasar da su guji amfani da karfi fiye da kima.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!