Labarai
Tinubu ya cire sunan Maryam Shattima daga jerin sunayen Ministocinsa

Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan Dr. Mairiga Mahmud domin maye gurbin Maryam Shetty daga Kano wadda aka tura sunanta a ranar Larabar data gabata.
Tinubu ya aike da sunayen ne ta cikin wata wasika da ya aikewa majalisar dattawa kuma Shugaban majalisar Godswill Akpabio ya Karanta a zaman majalisar na yau juma’a
Haka zalika Bola Ahmad Tinubun ya aikewa majalisar dattawa sunan tsohon Ministan ƙwadago na kasa Festus Keyamo domin amincewa da shi don nada shi a matsayin minista.
You must be logged in to post a comment Login