Connect with us

Labaran Wasanni

Tokyo 2020: AFN ta bude sansanin daukar horo a Abuja

Published

on

Hukumar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle ta Najeriya, AFN, ta bude sansanin horas da ‘yan wasan da za su wakilci kasar nan a gasar Olympics ta 2020.

An dai bude sansanin daukar horon ne a ranar Lahadi 4 ga watan Yuli a Abuja.

Babban Sakataren hukumar ta AFN, Adisa Beyioku, a cikin wata takarda da ya aikewa Daraktan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na ma’aikatar wasanni, ya gayyaci ‘yan wasa da masu horaswa zuwa sansanin.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, an gayyaci ‘yan wasa 25 da masu horaswa 10 don yin zango yayin da ake tunkarar wasannin Tokyo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!