Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Tokyo Olympics: ‘Yan wasan Najeriya sun shiga sansanin daukar horo

Published

on

‘Yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na Najeriya sun fara shiga sansani daukar horo zagaye na biyu a yankuna uku na fadin kasar nan don shirya wa wasannin gasar Tokyo 2020 Olympic.

A cewar daraktan ‘yan wasan Simeon Ebhojiaye, ‘yan wasan za su kasance sansanin tsawon makonni uku a garin Port Harcourt da Abuja da kuma Yenogoa.

A garin Port Harcourt za a gudanar da wasan tsalle-tsalle da guje-guje na tsawon zagaye 14 karkashin masu horaswa biyu a sansanin yayin da a Abuja za a gudanar da wasannin masu bukata ta musamman inda ‘yan wasan kwallon Tennis 14 da masu daga kayan nauyi 8 suka kasance a sansanin.

Haka kuma akwai ‘yan wasan damben zamani guda 8 da suke a sansanin na garin Yenogoa dake jihar Bayelsa duk a karkashin masu horaswa biyu.

Ka zalika, a zagayen farko an kafa sansanin ne a makarantar horas da malamai dake a garin Pankshin a jihar Plateau inda ‘yan wasa 4 suka sami halartar sansanin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!