Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsafta muka fi baiwa fifiko a sana’ar mu –Masu lemo da Mangwaro

Published

on

Kungiyar masu sayar da Lemo da Mangwaro ta Kasuwar ‘Yanlemo a Kano tace suna tsaftace kayan marmarin da ake siyarwa ga mutane da kuma tsaftar kasuwar domin kare lafiyar al’umma daga kamuwa da cututtukan zamani.

Shugaban kungiyar kasuwar masu sayarda Lemo da Mangwaro Alhaji Mustafa Idi ne ya bayyana haka a yayin zantawarsa da wakilin Freedom Radio Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa.

Karin labarai:

‘Yan kasuwa su kula da tsaftace wuraren sana’ar ku-Hussam Musa Kyari

Tabbas Afakallahu na kokari wajen tsaftace Kannywood –Kamaye

Alhaji Mustafa Idi ya kara da cewa sun dauki matakin tsaftace ciki da wajen kasuwar domin ganin basu baiwa kwayoyin cuta gurin zama ba musamman yadda hukumar kwashe shara ta jihar kano ke basu goyan baya don kwashe sharar kasuwar.

Shugaban kungiyar Alhaji Mustafa Idi ya kuma nanata cewa babu wani mutum guda da kungiya zata bari ya shigo da kaya mara kyau domin a sayarwa da mutane wanda a karshe zai iya cutar da lafiyar dubban jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!