Connect with us

Labarai

Tsaro: An sake sanya dokar hana zirga-zirga a Filato

Published

on

Gwamnatin jihar Filato ta sake sanya dokar takaita zirga-zirga na tsawon awanni ashirin da hudu a kananan hukumomin jihar na yankin Arewa.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Makut Macham ya fitar ta tabbatar da sanya dokar daga Larabar nan.

Sanarwar ta ce, dokar za ta fara aiki daga karfe hudu na yammacin yau, har zuwa sanarwa ta gaba da za a fitar.

Wannan ya biyo bayan samun rahoton harin yan bindiga a yankin Yelwar Zangam da ke kauyen Zangam, lamarin da yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu a daren jiya Talata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!