Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar hana zirga-zirga a wasu kananan hukumomi

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana zirga-zirga har tsawon sa’o I 24 a kananan hukumomin Zangon Kataf da garin Chawai da ke karamar hukumar Kauru.

Gwamnatin ta kuma ce dokar za ta fara aiki ne nan take.

Wannan na cikin wata sanarwa da kwamishinan harkokin cikin gida Samuel Aruwan ya fitar a ranar Alhamis.

A cikin sanarwar Samuel Aruwan ya ce hukumomin tsaro suna kokarin shawo kan matsalar tsaron da ta addabi yankunan a yanzu haka.

A makon da ya gabata ne aka samu barkewar rikici a Zangon-Kataf a kan wata gona, lamarin da ya haifar da fargaba a zukatan mazauna yankin.

A cewar kwamishinan, shugabannin al’ummar yankin sunyi kokarin shawo kan matsalar, sai dai hakan ya gagara, lamarin da ya sanya gwamnatin jihar daukar matakin hana zirga-zirga.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!