Connect with us

Labarai

Gwamna Mutfwang ya sanya dokar takaita zirga-zirga

Published

on

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya saka  sababbin matakan kariya na takaita zirga-zirga a wasu sassan jihar, biyo bayan kashe kashen al’umma da aka yi a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar a  shafinsa na  X, inda ya bayyana harin a matsayin kisan gilla da ake kai wa jihar da gangan, yana mai cewa  jihar ta Filato ba za ta rushe ba.

Daga cikin matakan da aka dauka  akwai haramta kiwon dabbobi da daddare a fadin jihar baki daya, kana  gwamnati ta hana jigilar shanu bayan karfe 7:00 na yamma, sannan an takaita zirga-zirgar babura daga karfe 7:00 na yamma zuwa 6:00 na safe a fadin jihar.

Gwamnan  ya bayyana alhinin sa  kan harin da aka kai kauyen Zikwe da ke karamar hukumar Bassa a daren Lahadi, 13 ga Afrilu, wanda harin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da jimamin rasa sama da rayuka 50 a wani mummunan hari da aka kai garin Bokkos  lamarin da ya jefa jihar  cikin tashin hankali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!