Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Tsaro: Buhari zai gana da sakataren harkokin wajen Amurka

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yi wata ganawa ta musamman da sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken.

Rahotanni sun ce shugaba Buhari zai gana da mista Blinken ta kafar internet a gobe talata.

Wannan dai ita ce tattaunawa ta farko da mista Blinken zai yi da shugabannin nahiyar afurka tun bayan kama mulkin shugaba Joe Biden

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatan harkokin wajen Amurka Ned Price ya fitar, ta ce, yayin tattaunawa tsakanin sakataren harkokin wajen na Amurka da shugaba Buhari za a mai da hankali ta bangarorin kulla alaka kan mulkin dimukuradiya, tsaro da kuma tattalin arziki.

Haka zalika sanarwar ta kuma ce sakataren harkokin wajen na Amurka zai kuma gana da shugaba Uhuru Kenyatta na Kenya bayan ganawa da shugaba Buhari da ministan harkokin wajen kasar nan Geoffrey Onyeama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!