Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsoffin dalibai su rika tallafawa makarantunsu – Sarkin Kano

Published

on

Daga Safarau Tijjani Adam

 

Mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce dole ne sai tsoffin dalibai sun taimakawa bangaren ilimi a kasar nan, la’akari da yadda gwamnatin kadai bazata wadatar ba.

 

Sarkin na Kano na bayyana haka ne yayin da yake jawabi a wajen taron bikin cika shekara 30 na tsoffin daliban makarantar ‘yan mata ta Sumaila SOGA aji na 1990.

 

Sarkin wanda Fagacin Kano Alhaji Habibu Bello Dankadai ya wakilta, ya bukaci tsoffin daliban na Sumaila da su rika taimakawa makarantar tasu ta fannin ci gabanta don tabbatar da samun ilimi mai nagarta ga daliban yanzu.

 

Shugabar kungiyar Hajiya Halima Ibrahim ta ce, da ma kudirin kungiyarsu shi ne su tallafawa makarantar ta dora su a tafarkin da suke kai a yanzu.

 

Tana mai cewa, tuni suka fara tallafawa makarantar da gyaran wasu sassanta da kuma kayan koyo da koyarwa.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!