Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ya zama wajibi dalibai su jajirce don neman ilimi – Jami’ar Maryam Abacha

Published

on

Jami’ar Maryam Abacha dake Maradi Dakta Bala Muhammad Tukur ya yi kira ga dalibai dake karatu a jami’o’i da su mai da hankali kan karatun su don su zama al’ummar da za’ yi alfahari dasu a kasar nan.

Daraktan hadin gwiwa da kulla alaka na Jami’ar Maryam Abacha Dake Maradi, Dakta Bala Muhammad Tukur ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin barka da hantsi na nan gidan radio freedom da ya gudana a safiyar yau.

Bala Muhammad yace yana da kyau iyayen dalibai su kara zage dantse wajan biyan kudaden makarantar ‘’ya’yan su, wanda da shi ne jami’ar ke gudanar da harkokin koyo da koyar wa.

An bukaci a daga darajar kwalejin ilimi ta Nasiru Kabara zuwa jami’a

Dokar kafa hukumar bunkasa ilimi na jihar Kano ya tsallake karatu na 2

Gwamnatin kano za ta kafa hukumar cigaban ilimi

Dakta Bala Muhammad ya kuma ce jami’ar a yanzu haka zata cigaba da wasu kwasa-kwasan da ta dakatar domin ganin an bunkasa harkar koyarwa dan ci gaban daliban jami’ar.

Daraktan ya kuma ce babban abin jin dadin shine daliban dake karatu a jami’ar sun fito ne daga kasar nan duk da cewa a jamhuriyar Nijar take.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!