Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yadda aka yi bikin ranar wanzar da zaman lafiya ta duniya a Kano

Published

on

Masanin halayyar dan Adam dake jami’ar Bayero a nan Kano, ya bayyana rashin zaman lafiya da cewa daya ne daga cikin Abubuwan da ke hana tattalin arzikin kasa bunkasa.

Dakta Maikano Madaki shi ne ya bayyana hakan ne yayin zantawarsa da wakiliyarmu Aisha Aminu Kundila a wani bangare na bikin ranar kauracewa tashe-tashen hankula ta duniya da ake gudanarwa a yau.

Ya ce, ranar na mayar da hankali wajen tunawa da wadanda Suka yi yaki kan kauracewa tashin hankali a dadin duniya tare da fito da sabbin dabaru na tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Majalisar Dunkin duniya ce dai ta ware duk ranar biyu ga watan oktobar kowacce shekara don karrama shugaban kasar India Mahat Maghandi Wanda ya jagoranci samun yancin Kai da zaman lafiya a kasar ta India.

Muna dauke da cikakken rahoton bikin ranar a labaran mu na gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!