Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba siyasa ce zata sa mu shimfida layin dogo ba – Buhari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce bunkasar tattalin arzikin kasar nan shi ne dalilin da ya sanya ta ke kokarin shimfida layin dogo daga Kano zuwa Maradi a jamhuriyar Nijar, ba batun siyasa ba kamar yadda wasu ke yadawa.

Ministan sifiri Rotimi Amaechi ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai jiya a Abuja.

Ya ce, ba daidai bane wasu al’ummar kasar nan su rika sa batun siyasa cikin aikin da ya ce ba shakka zai taimaka wajen bunkasar tattalin arzikin Najeriya.

Rotimi Amaechi ya ce ba ya ga samar da aikin yi, jirgin kasar zai kuma taimaka wajen bunkasa shige da ficen kayayyaki tsakanin kasashen biyu.

Ministan sifirin ya kara da cewa, gwamnatin ta dau wannan mataki ne biyo bayan nazartar yadda ake samun gasa tsakanin tashoshin jiragen ruwa da ke makwabtaka da kasar nan.

Har ma ya buga misalin cewa musamman na jamhuriyar Benin da Togo da kuma Ghana, wanda shimfida layin dogon zai sa ‘yan kasuwar Nijar su karkatar da akalar kayayyakinsu zuwa tashoshin jiragen ruwan Najeriya.

 

 

AI

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!