Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yadda kafofin sada zumunta ke ingiza matasa tsallakawa kasashen waje – IOM

Published

on

Hukumar kula da masu kaura ta duniya IOM ta ce kafofin sada zumunta na zamani ne ke ingiza matasan kasar nan wajen ganin sun tsallaka kasashen waje domin samun rayuwa mai inganci.

Babban jami’in hukumar a Najeriya Mr Frantz Celestin ya bayyana hakan yayin taron manema labarai game da rawar da kaurar jama’a ke takawa kan kalubalen tsaro a duniya.

Ya ma buga misali da ‘yan Najeriyar da suka dawo daga kasar Libya, wadanda mafi aksarinsu sun fito ne daga Jihohin kudancin kasar nan.

Mr Celestin ya ce labaran da ake wallafawa a shafukan sada zumunta na zamani kan irin daular da ake shiga a kasashen waje musamman Turai ne ke tunzura matasan har su sanya burin zuwa can.

Ya kara da cewa duk da malolin tsaron da ake fuskanta a yankin arewa maso gabashin kasar nan a shekarun nan, kididdiga ta nuna cewa hakan bai sanya matasa masu yawa sun yi kwadayin ketarawa kasashen wajen ba.

Jihohin da aka fi samun matasa masu haurawa kasashen waje daga kasar nan sun hadar da Edo da Delta da Lagos da Imo da kuma Ogun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!