Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: Buhari zai dawo da ‘yan Najeriya mazauna kasar China

Published

on

Ofishin jakadancin kasar nan da ke birnin Beijing a kasar China, ya Ce, gwamnatin tarayya ta kammala shirye-shirye domin fara jigilar yan kasar nan mazauna can domin dawo da su gida Najeriya.

A cewar ofishin daukar wannan mataki ya biyo bayan fitar wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ya nuna yadda hukumomi a

birnin Guangzhou suka fatattaki wasu ‘yan kasuwar kasar nan da dalibai da ke karatu a can kasar ta China daga dakunan Otal dinsu.

Rahotanni sun ce birnin Guangzhou shine gari da al’ummar Afirka suka fi ziyarta domin gudanar da harkokinsu na kasuwanci a kasar ta China.

LABARAI MASU ALAKA

Yadda cutar Corona Virus ta shafi ‘yan Najeriya a kasar China

Covid-19: Buhari zai rabawa al’ummar Kano sama da naira biliyan daya

Covid-19: Coronavirus na iya kawo karayar tattalin arziki a Najeriya -Buhari

A cikin faifan bidiyon dai al’ummar Najeriyar sun yi ikirarin cewa bayan fatattakar su daga masaukan nasu da hukumomin birnin su ka yi, basu samar musu da wani waje na daban ba, sannan ba a basu abinci ba.

Wani dalibi dan asalin kasar nan wanda yana daya daga cikin wadanda lamarin ya shafa, ya shaidawa gidan talabijin na BBC cewa, akwai ‘yan kasar nan sama da dari watse akan tituna babu abinci babu masauki.

Ko a shekaran jiya Alhamis ministan harkokin kasashen waje na kasar nan Geoffrey Onyeama ya shaidawa manema labarai cewa ya gayyaci jakadan kasar ta China a Najeriya, Mr. Zhou Pingjian domin jin dalilan da ya sa hukumomi a birnin na Guangzhou su ka ji zarafin al’ummar kasar nan mazauna can.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!