Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

‘Yan bindiga sun kashe mutane 20 a Dafur

Published

on

A karon farko cikin shekaru da dama ‘yan bindiga sun kashe mutune 20, ciki har da yara kanana a yankin Dafur na kasar Sudan da yaki ya dai-dai-ta.

Wani shugaban ‘kabila ya bayyana cewa wannan na zuwa ne biyo bayan cimma wata yarjejeniya da masu gonaki cewar za su koma bakin aikin su na noma, sai dai a yammacin jiya ne ‘yan tada kayar baya suka bude musu wuta tare da kashe mutane 20 ciki har da mata da kananan yara.

Lamarin ya faru ne a yankin Aboudous dake nisan kilomita 90 daga kudancin Nyala, babban birnin kudancin lardin Darfur.

A shekarar 2003 ne rikici ya barke a yankin Dafur tsakanin kabilu ‘yan tsiraru da ‘yan tawaye masu biyayya ga tsohon shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al-Bashir.

Majalisar dinkin duniya ta ce rikicin na yankin yayi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da dubu 30, kana kuma ya raba miliyan 2 da rabi da muhallansu.

A cikin watan Afrilun shekarar 2019 ne aka hambarar da gwamnatin shugaba Omar Al-Bashir, biyo bayan watanni da aka kwashe ana zanga-zangar kin jinin gwamnatinsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!