Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

‘Yan kasuwa sun nemi Ganduje ya bude Kasuwanni sau biyu a mako

Published

on

‘Yan Kasuwa sun  bukaci gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da ya duba dokar kulle na zaman gida tare da bada dama ga ‘yan Kasuwannin Sabongari da Kwari da na  Singer domin fitowa Kasuwancin su a kebabbun ranakun  da aka ware a mako don gudanar da nasu Kasuwancin.

Alhaji Imamu Tafida, Tafidan Dakayyawa kuma daya daga cikin Dattijan Kasuwar Muhammad Abubakar Rimi, wato Sabongari shi ne yayi wannan kira duba da mawuyacin halin da ‘yan Kasuwan suke ciki kamar yadda jagororin  Kasuwar suka tabbatar.

Alhaji Imamu Tafida, ya ce ‘yan kasuwa da dama, sun tafka asara ta miliyoyin nairori sakamakon rufe kasuwannin, kasancewar kayan da suka siyo basu shigo ba dalilin hana shige da fice, hakazalika wanda ake dasu a kasuwar ba a siyar dasu ba.

Tafidan Dakayyawan, ya kuma bada tabbaci ga gwamnati na cewar zasu yi duk mai yiwuwa wajen daukar matakan kariya daga cutar ta Corona daga bangaren su da masu mu’amala dasu da zarar an basu damar gudanar da Kasuwancin su.

Wakilin mu, Aminu Halilu Tudunwada, ya ruwaito mana cewa, Alhaji Imamu Tafida, ya bukaci al’umma dasu bi umarnin hukumomi da ma’aikatan lafiya, tare da rubanya addu’a domin ganin an kawar da wannan annoba da ta kawo tsaiko a al’amuran yau da kullum na jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!