Connect with us

Labarai

‘Yan sanda a jihar Kwara sun hallaka ‘yan bidiga bayan yunkurin kai hari

Published

on

Rundunar ’yan sandan jihar Kwara ta tabbatar da kashe ’yan bindiga mutum biyu a harin da suka kai garin Eruku da ke ƙaramar hukumar Ekiti a ranar Talata. Harin ya tayar da hankula a yankin, inda mazauna yankin suka tabbatar da jin ƙarar harbe-harben maharan.

 

Sai dai an sha rabuwar kai tsakanin rahotanni dake fitowa dangane da harin, inda Wasu rahotanni suka nuna cewa maharan sun yi niyyar kai hari kan wata coci, yayin da wasu kuma suka ce sun shigo ne domin garkuwa da mutane kamar yadda suke yi a kai a kai.

 

Ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Toun Ejire-Adeyemi tayi ta tabbatar da cewa mutum biyu sun mutu a harin, yayin da ɗan kungiyar sa-kai guda ya jikkata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!